Home LabaraiTinubu ya ɗaga darajar Bianca Ojukwu zuwa ministar harkokin wajen Najeriya
Tinubu

Tinubu ya ɗaga darajar Bianca Ojukwu zuwa ministar harkokin wajen Najeriya

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya naɗa Bianca Odumegwu-Ojukwu a matsayin ministar harkokin wajen ƙasar, bayan murabus ɗin Yusuf Tuggar, wanda ya ajiye mukaminsa domin shiga takara a zaɓen 2027.

Bianca ita ce ƙaramar minista a ma’aikatar kafin wannan sabon matsayin.

Kamar yadda wata sanarwa daga mai magana da yawun shugaban ƙasar, Bayo Onanuga, ta bayyana, an kuma naɗa Sola Enikanolaiye a matsayin ƙaramin minista a ma’aikatar, inda za a jira amicewar majalisar dattawa.

Rasha za ta rage girman faretin sojinta na shekara-shekara saboda fargabar hari daga Ukraine

Kotu ta hana INEC amincewa da tarukan da ADC ta gudanar na tsagin David Mark

Kafin a naɗa shi muƙamin, Enikanolaiye wanda haifaffen jihar Kogi ne, shi ne babban mataimaki na musamman ga shugaba Tinubu kan harkokin ƙasashen waje.

Related Articles

Leave a Comment

Prove your humanity: 4   +   1   =